Legit Hausa
Munir Sanusi, Shugaban ma’aikatan Sarkin Kano, Muhammadu
Sanusi II, yace masarautar na nazari akan irin abunda ke kunshe a takardar da
aka aiko wa sarkin. Ofishin sakataren gwamnatin jihar ta aike da takardar neman
ba'asi kan tuhumar da ake yi wa sarkin na yin bushasha da makudan kudaden
masarauta a madadin Gwamna Abdullahi Ganduje.
Wata majiya ta ruwaito cewa ana zargin masarautar da yin
fakaca da kudade. Shugaban ma’aikatan ya tabbatar da karban wasikar, cewa an
bukaci sarki da ya bayar da amsa cikin sa’o’i 48. “Mun karbi takardar neman
ba'asi a yau (Alhamis).
Gwamnatin ta nemi samun amsa cikin sa’o’i 48 daga mai
martaba. Fada na nazari akan abunda takardar ya kunsa,” inji shi. A baya
Legit.ng ta rahoto cewa tataburza dake tsakanin gwamnatin jahar Kano da fadar
masarautar Kano ta kara zafafa, inda a yanzu Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya
kaddamar da tsare tsaren tsige mai martaba Sarki Muhammadu Sunusi II daga
kujerar sarauta.
Majiyarmu ta ruwaito gwamnan ya aika ma Sarki wata takarda
dake kunshe da dukkanin tuhume tuhumen da gwamnati ke masa dangane da
almubazzarancin kudade, inda ya bukaci ya bashi amsa cikin sa’o’I 24.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Tags:
LABARI