Legit Hausa
Yan bindigan da suka yi garkuwa da yara biyu a watan da ya
gabata a kauyen Dan-Ali da ke jihar Katsina a jiya Alhamis, sun fada ma
iyayensu cewa an kashe yaran a lokacin da rundunan sojin sama ta kai hari.
Mahaifinsu yace maimakon a sako su bayan sun karbi kudin fansa naira N2.5
million, yan bindigan sun jagorance shi zuwa kabarurrukan yaransa.
Anyi garkuwa da Anas Idris da Ibrahim Idris da misalin karfe
1:30 na tsakar dare a ranar 27 ga watan Mayu a lokacin da suka kai hari gidan.
Yan bindigan sun bukaci naira miliyan Miliyan 20 a matsayin kudin fansa wanda
daga baya an bada naira miliyan 2.5.Mahaifinsu, Alhaji Idris Garba Dan Ali, a
wani hiran shi da manema labarai yace:
“Naje domin na hadu dasu (Yan bindigan) a kauyen Leletu na
karamar Hukumar Dan Musa. Suka ce in jira su na dan lokaci. Bayan dan lokaci
kadan, su shida suka zo sannan bayan sun karbi kudin, suka bukaci in fada musu
wanda nazo ceto.
“Sai suka fada mani cewa yan kwanaki da suka gabata rundunar
sojin sama sun gudanar da aikin tayar da yankin kuma cewa an kashe yarana a
harin. Sai suka nemi na bisu domin ganin kabarinsu, amma naki sannan na fada
masu cewa tunda an kashe su, na bar komai a hannun Allah kuma Allah ya ji kansu
da rahma.”
Wani Jami’in sojin sama wanda yayi magana bisa sharadin ba
za a bayyana sunansa ba ya karyata zargin da yan fashin suka yi, na cewa
rundunan ce ta kashe yaran a harin da suka kai ma yan fashin a jejin.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi