Legit
Hausa
A daren
Lahadin da ta gabata ne tsohon sakataren gwamnatin Tarayya, Alhaji Yayale
Ahmed, ya gargadi gwamnatin jihar Kano da ta tabbatar da yin taka tsan-tsan
yayin gudanar da binciken a kan Sarkin Kano, Mai Martaba Muhammad Sanusi II.
Tsohon
sakataren gwamnatin kasa ya nemi gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin
gwamna Abdullahi Umar Ganduje, da ta tabbatar ba ta sabawa ka'ida ta shari'a ba
a yayin takaddamar Masaurautar Kano da wargi ba ya kusantar ta.
Yayale
wanda ya kasance tsohon shugaban ma'aikata gwamnatin Tarayya kuma tsohon
Ministan Tsaro, ya ce duk da goyon bayan jam'iyyar adawa ta PDP, gwamnatin
jihar Kano ta tuna cewa Sarki Sanusi ya kasance uba ga dukkanin al'ummar jihar.
Yayin
ganawar sa da manema labarai ta hanyar wayar tarho, tsohon Ministan ya kuma
tunatar da gwamna Abdullahi Umar Ganduje cewa ya kasance jagora ga dukkanin
al'ummar jihar Kano duk da sabani na ra'ayin siyasa.
Yawale
wanda shi ne mai rike da rawanin Ajiyan Katagum, ya gargadi gwamnatin Kano kan
cewa muddin ta ci gaba gudanar da al'amura tare da mu'amalantar masarautar Kano
kamar yadda ta ke yi a yanzu, babu shakka ba za a kwashe lafiya ba cikin
ilahirin Arewacin Najeriya baki daya.
Ana iya
tuna cewa gwamnatin Kano na zargin fadar Mai Martaba Sarki Sanusi da almundahar
kimanin Naira biliyan 3.4 na masaurautar Kano. Sai dai yayin mayar da martani
fadar ta ce abin da ta riska yayin cin gajiyar mulki bai wuce Naira biliyan 1.8
ba.
Jaridar
Legit.ng ta ruwaito cewa, fadar shugaban kasa Muhammadu Buhari ta kafa kwamitin
wasu gwamnoni hudu na jihohin Ekiti, Kebbi, Jigawa da kuma na Neja akan shiga
tsakani tare da tabbatar da sulhu tsakanin gwamna Ganduje da kuma Sarki Sanusi.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi