Manyan ma'aikatan gwamnati za su shiga yajin aiki nan da kwana 7

Manyan ma’aikatan gwamnati karkashin kungiyar manyan ma’aikatan gwamnati (ASCSN) ta ce za ta shiga yajin aiki sakamakon karya dokar ma’aikatan gwamnati da yarjejeniyar da suka kulla da hukumar inshora ta Najeriya (NAICOM). ASCSN ta ce sharuddan yarjejeniyar da aka rattafa ma hannu a ministirin kwadago a cikin watan Agusta na 2018, sun hada da samar da kudin alawus na man fetur da dizil, da kuma ba sauran ofisoshi mahimmanci. Kungiyar ta ce zata shiga yajin aikin idan hukumar ba ta zartar da sharuddan yarjejeniyar ba nan da kwana bakwai. A jawabin da sakataren kungiyar, Isaac Ojemheken, ya sanyawa hannu, ASCSN, ta ce “Muna a matse shi ya sanya muke sanar maku cewa mambobin kungiyar ASCSN ta yi taro a Abuja a ranar 24 ga watan Yuni 2019, kuma an cimma matsaya cewa a ba hukumar inshora wa’adin kwana bakwai don ta tabbatar da yarjejeniyar da ta kulla da kungiyar mu.” “Ya zama dole mu sanar cewa ASCSN ba ta da laifi idan har aka shiga yajin aiki sakamakon rashin biya ma yan kungiyar bukatunsu cikin kwana bakwai.” “Haka zalika, ya zama dole mu sanar cewa babban sakataren ministirin kwadago da aiki, babban sakataren ministirin kudi, babban daraktan yan sandan cikin gida (DSS), babban sifeton yan sanda, da shugaban hukumar inshora duk sun sanya hannu a wannan takarda." “Muna cikin rashin jin dadi muke bayyana maku cewa bayan shekara biyu da cimma yarjejeniyar farko a ranar 26 ga watan Satumba 2017, hukumar ta inshora ta ki tabbatar da yarjejeniyar da gan gan duk da rokon da aka yi masu." Read more: https://hausa.legit.ng/1245706-yajin-aiki-maaikatan-gwamnatin-tarayya-sun-ba-da-waadin-kwana-7.html

Legit Hausa

Manyan ma’aikatan gwamnati karkashin kungiyar manyan ma’aikatan gwamnati (ASCSN) ta ce za ta shiga yajin aiki sakamakon karya dokar ma’aikatan gwamnati da yarjejeniyar da suka kulla da hukumar inshora ta Najeriya (NAICOM). ASCSN ta ce sharuddan yarjejeniyar da aka rattafa ma hannu a ministirin kwadago a cikin watan Agusta na 2018, sun hada da samar da kudin alawus na man fetur da dizil, da kuma ba sauran ofisoshi mahimmanci.

Kungiyar ta ce zata shiga yajin aikin idan hukumar ba ta zartar da sharuddan yarjejeniyar ba nan da kwana bakwai. A jawabin da sakataren kungiyar, Isaac Ojemheken, ya sanyawa hannu, ASCSN, ta ce “Muna a matse shi ya sanya muke sanar maku cewa mambobin kungiyar ASCSN ta yi taro a Abuja a ranar 24 ga watan Yuni 2019, kuma an cimma matsaya cewa a ba hukumar inshora wa’adin kwana bakwai don ta tabbatar da yarjejeniyar da ta kulla da kungiyar mu.”

“Ya zama dole mu sanar cewa ASCSN ba ta da laifi idan har aka shiga yajin aiki sakamakon rashin biya ma yan kungiyar bukatunsu cikin kwana bakwai.” “Haka zalika, ya zama dole mu sanar cewa babban sakataren ministirin kwadago da aiki, babban sakataren ministirin kudi, babban daraktan yan sandan cikin gida (DSS), babban sifeton yan sanda, da shugaban hukumar inshora duk sun sanya hannu a wannan takarda."

 “Muna cikin rashin jin dadi muke bayyana maku cewa bayan shekara biyu da cimma yarjejeniyar farko a ranar 26 ga watan Satumba 2017, hukumar ta inshora ta ki tabbatar da yarjejeniyar da gan gan duk da rokon da aka yi masu."
 

DAGA ISYAKU.COM

 Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN