Majalisar dokoki ta tara: Na hango tarin bala’i da ke tunkarowa - Ndume


Legit Hausa

Tsohon shugaban masu rinjayi a majalisar dattawa, Sanata Ali Ndume, a ranar Alhamis, 6 ga watan Yuni ya bayyana cewa dole majalisar dattawa na tara tayi aiki don kare yancin ta don gujewa rigingimu a zaman majalisar. Sanatan mai wakiltan Borno ta kudu ya bayyana cewa abu guda da ya kamata kowace majalisa ta kasance da shi ita ce yanci wacce zata yi iya kokarinta wajen kare wannan yancin. 

Ndume wanda ya kasance daya daga yan takara dake kan gaba a wajen neman shugabancin majalisar dattawa yayi magana yayinda yake bada gudumuwar shi a taron bankwana na majalisar dattawa ta takwas. Ya bayyana cewa banbancin dake tsakanin damukardiyya da kuma gwamnatin soja shine yancin majalisar dokoki. 

Ya dage cewa dole a girmama majalisar a matsayin alamar damukardiyya wacce dole a kare yancinta a dukkan lokuta. Ya bayyana cewa majalissan ta kasance ginshikin damukardiyya a kowace kasa. A baya Legit.ng ta rahoto cewa Sanata Ali Ndume, ya ce ba zai janye takarar sa ba yayin babban zaben da za a gudanar a ranar 11 ga watan Yuni a zauren majalisar dake garin Abuja.

Ndume wanda ya bayyana hakan yayin ganawar sa da manema labarai a ranar Alhamis, ya ce ba ya bukatar kai wa shugaban kasa Muhammadu Buhari wata ziyara domin sauya ra'ayin sa na janye takarar neman shugabancin sabuwar majalisar dattawan kasar nan. 

Kamar yadda jaridar The Punch ta ruwaito, Sanata Ndume ya ce ba ya da wata bukatar neman shawarar shugaban kasa Buhari domin yanye takara ga Sanata Ahmed Lawan wanda ya kasance daya daga cikin masu hankoron kujerar jagoranci a majalisar dattawa.
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN