Legit Hausa
Lai Mohammed, tsohon minstan labarai, a ranar Laraba, ya ki
bayyana a gaban Mai shari’ah Folashade Ogunbanjo Giwa na babbar kotun gwamnatin
tarayya dake Abuja, don yayi bayani akan kudi Naira biliyan 2.5 da aka baiwa
kamfanin Pinnacle Communication.
A zaman na ranar Laraba, an cigaba da sauraren karar da ake
yima babban darakta na watsa labarai, Ishaq Kawu Modibbo, da kamfanin Pinnacle
Communication da wasu mutum biyu. Tsohon ministan na labarai, na cikin sunayen
da mai gabatar da kara, Henry Emore ya bayar a matsayin shaidun hukumar hana
ta'annaci da kudin kasa (ICPC) kuma ana tsammani zai bayyana gaban kotu don ya
bayar da shaida a matsayinsa na tsohon minista da ya bayar da umurnin a biya
2.5 ga kamfanin Pinnacle.
Amma, bayan da ya kira shaidu biyu, mai gabatar da karan ya
gaya ma kotu cewa ya so ya kira shaidarshi na gaba, tsohon ministan labarai
amma bai samu halartar zaman kotun ba. Emore ya bayyana ma kotun cewa Lai
Mohammed yayi tafiya zuwa kasar waje amma ana tsammanin zai dawo Najeriya kafin
ranar 31 ga watan Yuli.
Haka zalika ya bayyana ma kotu cewa Lai Mohammed ya bayar da
shaidarshi a rubuce ga ICPC, a matsayinshi na tsohon minista. Mai gabatar da
karar ya kuma bayyana ma kotu cewa sauran shaidun da ya so ya kira sunyi tafiya
zuwa kasar Saudiyya.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi