Ku karbe ragamar shugabanci a sarar - Obasanjo ga matasa


Legit Hausa

Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo jiya Alhamis, 27 ga watan Yuni, ya bukaci matasa da su nemi takarar mukaman shugabanci a kasar. Yayin da ya karbi bakuncin mambobin kungiyar matasan Najeriya a gidansa da ke harabar dakin karatunsa a Abeokuta, Obasanjo ya ce: “kada ku bari kowa ya fada muku cewa kun yi kankanta da neman shugabanci, na soma bada gudumuwana a duniya a lokacin da nake aiki a kasar Congo a shekarar 1960, a lokacin ina dan shekaru 24.

"A lokacin da na tafi filin daga na kasance dan kasa da shekara 35, a lokacin ne na zama shugaban kasa a mulkin soja, ban kai shekaru 40 ba a lokacin." Obasanjo ya nuna damuwa cewa sama da yara miliyan 13 ne basa zuwa makaranta a Najeriya. Yace: “duk abin da nayi, nayi ne saboda na kasance mai ilimi kuma mai kishin kasar Najeriya.

“Da banyi karatu ba da ban kai matsayin yin abubuwan da nayi ba, a yau ina matukar bakin cikin cewa fiye da yaran Najeriya miliyan 13 wadanda ya kamata suna a makaranta sun bar makaranta.”
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN