Kotun sauraron korafin zabe ta yi watsi da wata bukatar Buhari da INEC


Legit Hausa

Kotun sauraron korafin zaben shugaban kasa ta yi watsi da bukatar hukumar zabe ta kasa (INEC) da shugaban kasa, Muhammadu Buhari, na neman kotun ta kori karar da jam'iyyar PDM ta shigar a gaban ta. Buhari da INEC, kasancewarsu cikin wadanda jam'iyyar ke kara, sun bukaci kotun ta kori karar ne bisa dogaro da cewa ba ta shigar korafin ta a gaban kotun bisa ka'ida ba, kamar yadda doka ta tanada.

 Babban alkalin kotun, Jastis Mohammed Garba, ya ce jam'iyyar PDM ba ta saba wata ka'ida ba a karar da ta shigar. Ya ce PDM ta gabatar da dukkan wasu korafe-korafe tare da kalkale komai a ranar 15 ga watan Afrilu, wanda ya kasance cikin wa'adin da aka tsayar na kammala gabatar da korafi kafin ranar 21 ga watan Afrilu.

Jastis Garba ya kara da cewa jam'iyyar PDM ta bi tsarukan da dokokin zabe suka tanada, a saboda haka INEC da shugaba Buhari basu fahimci yadda lamarin ya ke ba.
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN