Legit Hausa
A ranar Litinin ne wata kotun sauararon kararrakin da suka
shafi fyade da rigingimun cikin gida da ke Ikeja a jihar Legas ta bayar da
umarnin tsare wani malamin Islama, Abdulsalam Salaudeen, bayan an gurfanar da
shi a gabanta bisa zarginsa da aikata fyade ga wata karamar yarinya mai shekaru
biyar a cikin Masallaci. Alkalin kotun, Jastis Abiola Soladoye, ya amince da
bukatar mai gabatar da kara na neman a tsare mai laifin. Bayan ya amsa bukatar
mai gabatar da karar, Soladoye ya daga fara sauraron karar zuwa ranar 14 ga
watan Oktoba.
Kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) ya rawaito cewar
ana tuhumar Salaudeen, mai shekaru 43, da laifin aikata fyade ga wata karamar
yarinyar da ke karkashin kulawarsa. Mai gabatar da kara, T. Olanrewaju-Dawodu,
ta shaida wa kotu cewa Salaudeen ya aikata laifin ne a ranar 22 ga watan
Disamba na shekarar 2018 a harabar Masallacin Olorunbabe da ke lamba 15 a titin
zuwa fadar unguwar Igando da ke daura da Legas.
Olanrewaju-Dawodu, ta ce an kama Salaudeen, wanda aka fi
kira da Alfa (Liman da harshen Yoruba), ta hanyar amfani da na'urorin daukar
hoton bidiyo da wasu mutane da ke zarginsa suka dasa a harabar Masallacin. Sai
dai, Salaudeen, mazaunin gida mai lamba 16 a kan titin Awoyemi da ke unguwar
Ikotun, ya musanta tuhumar da ake masa. Mai gabatar da kara ta ce laifin
Salaudeen ya saba da sashe na 137 na kundin manyan laifuka na jihar Legas,
wanda aka kirkira a shekarar 2015.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Tags:
NISHADI