Ko mai yayi zafi: Malami ya rataye kanshi a Kano


Legit Hausa

Jami'an hukumar 'yan sandan jihar Kano sun bada sanarwar mutuwar wani malamin makaranta, mai suna Femi Oguntumi dake zaune a unguwar Dakata, wanda aka tabbatar da cewa ya kashe kanshi ne. Mutumin mai shekaru 40 a duniya, wanda yake ma'aikaci ne a Kwalejin Karish, dake unguwar Kawaji, an iske shi ya rataye kanshi a jikin rufin dakin shi.

Mai magana da yawun hukumar 'yan sandan jihar, DSP Haruna Abdullahi, ya tabbatarwa da manema labarai faruwar lamarin, ya ce yanzu haka sun kai gawar marigayin asibitin Murtala domin gabatar da bincike akan shi. Ya kara da cewa jami'an su sun fara gabatar da bincike akan dalilin da yasa Femi ya rataye kanshi.

Ba wannan ne karo na farko da ake samun irin wannan lamari na kisan kai ba, a lokuta da dama akan iske mutum ya sha guba ko ya rataye kanshi, inda wasu suke alakanta hakan da yawan damuwa da kuma bakin talauci da mutane ke fama dashi a wannan lokacin.
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN