Legit Hausa
Mambobin majalisar dokokin jihar Kano sun zabi Abdul'aziz
Gafasa a matsayin sabon Kakakin majalisar jihar a karo na tara. Zaben ya biyo
bayan sanar da fitowa takararsa da dan majalisar jam'iyyar PDP mai wakiltar
karamar hukumar Dala, Lawan Hussain yayi jiya Litinin a lokacin da suka gabatar
da zaman farko a dakin majalisar.
Gafasa ya taba shugabantar majalisar jihar a lokacin mulkin
tsohon gwamnan jihar Malam Ibrahim Shekarau, a yanzu ya samu goyon bayan
dukkanin mambobin jam'iyyar PDP su goma sha uku dake majalisar jihar. Majiya
mai karfi ta bayyanawa jaridar Premium Times cewa, sauran mambobin jam'iyyar
APC guda 18 sun zabi dan majalisa mai wakilatar karamar hukumar Doguwa.
Hakan ya bai wa Gafasa damar samun kuri'u 21, yayin da shi
kuma dan majalisa mai wakiltar Doguwa, wanda aka tabbatar da cewa shi gwamnatin
jihar ke goyon baya ya samu kuri'u 18. Haka kuma an zabi dan majalisa mai
wakilatar karamar hukumar Makoda, Hamisu Cigari, a matsayin mataimakin Kakakin
majalisa a karo na hudu.
Gafasa ya nuna farin cikinsa ga 'yan majalisar da zaben shi
da suka yi, sannan kuma yayi alkawarin ba zai watsa musu kasa a ido ba. Ya kuma
sha alwashin yin aiki da kowanne mamba na majalisar duk da cewa suna da
bambancin jam'iyya da wasu.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi