Legit Hausa
A ranar Laraba 12 ga watan Yuni, aka gudanar da bikin ranar
dimokuradiyar Najeriya bayan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da
sauya ranar da a baya aka saba gudanar da bikin ta a 29, ga watan Mayu.
Shugaban kasa Buhari ya gabatar da jawabai da dama musamman
inda alkiblar gwamnatin sa a wa'adi na biyu za ta fuskanta da kuma wurare da
sabuwar gwamnatin sa za ta mayar da hankali a kai. Mun kawo mu wasu jerin
muhimman jawabai da shugaban kasar ya gabatar yayin bikin ranar dimokuradiyya
da aka gudanar a dandalin Eagle Square na garin Abuja.
1. Ina mutunta harkokin gudanar wa na hukumar INEC Shugaban
kasa Buhari ya ce ba zai gushe ba wajen ci gaba da ganin kimar hukumar zabe ta
kasa mai zaman kanta INEC a sakamakon bajintar da nuna wajen tabbatar da zaben
nagari da ya tsarkaka daga duk wani nau'i na rashin gaskiya.
2. Ina godiya da samun goyon bayan na zabe na a matsayin
shugaban kasa karo na biyu Shugaban kasa Buhari ya kwarara yabo gami da godiya
ga dukkanin wadanda suka bayar da gudunmuwa wajen tabbatar da nasarar jam'iyyar
sa ta APC. Ya yi godiya ta musamman a kan wadanda ba gushe ba wajen jefa masa
kuri'a tun daga zaben 2003 kawowa yanzu.
3. Najeriya babbar kasa ce a duniya Buhari ya ce kasar
Najeriya tana gogayyar kafadar ta da wasu kasashen duniya inda alkalumman
majalisar dinkin duniya a kwana kwanan suka tabbatar da cewa akwai yiwuwar
adadin al'ummar kasar nan zai kai kimanin miliyan 411 daga yanzu zuwa shekarar
2050. Najeriya za ta kasance a mataki na uku ta fuskar yawan al'umma bayan
kasar Sin da kuma Indiya.
4. Najeriya ta ciri tuta a nahiyyar Afirka Buhari ya ce
kasar Najeriya ta ja ragama tare da rataya nauyin wanzar da zaman lafiya
musamman a kasashen dake makotaka da ita a nahiyyar Afirka. Ya bayar da misalin
kasashen Gambia, Zimbabwe, Mozambique, Namibia da kuma kasar Afirka ta Kudu.
5. Dole ne mu inganta hanyoyin sufuri na ruwa, titi, layin
dogo da kuma wutar lantarki a zamance A yayin da gwamnatin sa ta sha alwashin
ribatar dukiyar sa wajen bunkasa ci gaban kasa, Buhari ya ce akwai muhimmiyar
bukata ta inganta gine-ginen tituna, layin dogo, tashohin jiragen ruwa da na
sama da kuma wutar lantarki a zamanance.
6. Ba ni da wani buri face sadaukar da rayuwa ta wajen yiwa
Najeriya hidima Shugaban kasa Buhari ya ce ya shafe tsawon rayuwar sa wajen
yiwa Najeriya hidima tun bayan da mallaki hankalin kansa. Ya lissafa lunguna da
sakonni na kasar nan da ya yiwa Najeriya bauta da suka hadar da Kaduna, Legas,
Abeokuta, Makurdi, Fatakwal, Maiduguri, Ibadan, Jos da kuma Abuja.
7. Masu adawa ne kadai ke tantamar ci gaban da Najeriya ta
samu a gwamnati na Sabanin kalubale da kasar nan ta fuskanta na matsin tattalin
arziki da kuma rashin tsaro, Buhari ya ce gwamnatin sa babu ko shakka ta taka
rawar gani wajen samun nasarori da suka tabbatar da ci gaba a kasar nan.
8. Matukar kasar Sin da Indiya na ganin karan su ya kai
tsaiko a fagen ci gaba, ba za a bar Najeriya a baya ba Shugaban kasa Buhari ya
ce sabanin kalubale da kasar Indiya da kuma Sin suka fuskanta, a halin yanzu
sun kasance kan sahu na gaba cikin jerin kasashen duniya masu bugun gaba da
samun ci gaba. Ya ce hakan kuwa za ta kasance ga kasar Najeriya domin kuwa ba
za ta zamo koma baya ba.
9. Ina alfahari da kananan masana'antu da kuma kananan 'yan
kasuwa Shugaban kasa Buhari yace yana matukar alfahari da kananan 'yan kasuwa
da kuma masana'antu masu wadatar da kasar nan da har a wani sa'ilin ake fitar
da kayayyakin su zuwa kasashen ketare. Ya ce hakan yana bunkasa tattalin
arzikin kasar nan ba kadan ba.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi