Legit Hausa
Alhaji Abba Anwar, Sakataren yada labarai na gwamnan Kano
Abdullahi Umar Ganduje ya ce ba ayi sulhu ba tsakanin gwamnan da sarkin Kano,
Muhammadu Sanusi II duk da cewa anyi taron a ranar Juma'a a Abuja.
Anwar ya bayyana hakan ne yayin wata sako da ya aike wa
Daily Trust. Ya ce, "Tabbas, Gwamna Fayemi da Alhaji Aliko Dangote sun
kira taron sulhu da Gwamna Ganduje da Sarki Sanusi suka halarta sai dai har
yanzu gwamnan bai bayyana matsayar sa kan batun ba.
"Abinda zan iya tabbatar muku shine har yanzu ana tattaunawa
saboda haka mu jira domin sanin matakin da gwamnan zai dauka." Ya kara da
cewa hakimai da yawa da sauran masu rike da sarautun gargajiya sun hallarci
taron.
A wani rahoton, Legit.ng ta ruwaito cewa Ganduje ya sake
nada Usman Alhaji a matsayin Sakataren Gwamnatin Jihar Kano da kuma Shehu
Mu'azu a matsayin babban akawun jihar Kano Sanarwan nadin na dauke ne cikin
wata jawabi da sakataren yada labarai na gwamna, Abba Anwar ya rabawa manema
labarai a ranar Laraba a Kano.
Ganduje ya yabawa ma'aikatan biyu bisa hidimar da su ka yiwa
jihar tare da shi a mulkinsa zango na farko da ya kare a ranar Laraba. Gwamna
Ganduje ya bukaci ma'aikatan biyu su aiki babu kama hannun yaro domin tabbatar
da cewa wannan mulkin ya fi na baya saboda alkawurran da ya yiwa al'umma.
An rushe dukkan masu rike da mukamman siyasa na jihar amma
banda wadanda ke da wa'addin aiki kamar yadda dokokin hukumomi da
ma'aikatatunsu suka tanada kamar yadda kamfanin dillancin labarai NAN ta
ruwaito.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi