Legit Hausa
Daga karshe, Shuugaba Muhammadu Buhari ya saka baki cikin
rikicin da ke faruwa tsakanin gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje da
Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II. An dade ana kira ga Shugaban kasar da
dattijan arewa su sasanta tsakanin gwamnan da Sarki duba da cewa rikicin na
daukan sabon salo.
Wata amintaciyar majiya daga fadar shugaban kasa ta shaidawa
Daily Nigerian cewa shugaban kasar baya jin dadin abinda ke faruwa a jihar Kano
sakamakon korafe-korafe da fargabar tabarbarewar tsaro.
"Ka san cewa shugaban kasa bai cika yin katsalandan a
harkokin jihohi ba. Amma kan wannan batun, ya zama dole shugaban kasa ya saka
baki," inji majiyar. "Shugaban kasa bai ji dadin yadda gwamnan ya
rarraba masarautar ba kuma da yunkurin da ya ke yi na tsige sarkin.
"Hakan ya sa shugaban kasan ya kira Ganduje a ranar
Alhamis kuma ya umurci Direkta Janar na DSS ya kira taron gaggawa da gwamnonin
jihohin Arewa maso Yamma. "Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ne ya
jagorancin gwamnonin bayan ya gana da shugaban kasar ya yi masa bayanni kan
halin tsaro a ranar Alhamis."
Daily Nigerian ta kuma ruwaito cewa shugaban kasar ya kira
sarkin zuwa taron gaggawa tare da Madakin Kano, Yusuf Nabahani a ranar Juma'a.
Idan ba a manta a ranar Laraba, Legit.ng ta ruwaito muku cewa Sarki Sanusi ya
soke Hawan Nassarawa bisa umurnin Gwamna Ganduje inda ya ce anyi hakan ne
saboda dalilan tsaro.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi