Da duminsa: Yadda aka rabawa 'yan majalisu cin hancin daloli domin su zabi Gbajabiamila


Legit Hausa

An samu kwararan shaidu dake nuna yadda aka dinga rabawa tsofaffin 'yan majalisar dokoki da sababbi kudi domin su zabi Femi Gbajabiamila a matsayin Kakakin majalisar wakilai ta kasa. 

Jaridar Sahara Reporters ta tabbatar da cewa an bai wa kowanne dan majalisa katin cire kudi, wanda aka sanya kudi masu tarin yawa a cikin kowanne, domin jawo hankalin su wurin zabar dan majalisar.
Duk da dai jaridar tace ba za ta iya saurin yanke hukunci akan ko nawa ne a cikin kowanne kati ba, amma tana da tabbacin cewa akwai makudan kudade a ciki. 

An raba katin ga wadanda tun farko suka nuna goyon bayansu ga Gbajabiamila, sannan kuma suka nuna suna tare dashi a kowanne hali. Kafin a fara gabatar da zaben Kakakin majalisar, an hango da yawa daga cikin 'yan majalisar a bangaren bandakin maza na majalisar suna raba daloli ga junansu. Idan ba manta ba kimanin 'yan majalisar tarayya 66 ne suka zabi Sanata Ahmad Lawan a matsayin shugaban majalisar dattawa, kuma anyi zargin cewa an bai wa kowannen su naira miliyan 25 domin su zabe shi.

 Gbajabiamila ya lashe zaben Kakakin majalisar da kuri'u 281, yayin da abokin hamayyarsa Umar Bago ya samu kuri'u 78.
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN