Ban yi danasanin abun da na aikata ba a Zamfara - Marafa


Legit Hausa

Sanata mai wakiltan yankin Zamfara ta tsakiya, Kabiru Garba Marafa, ya bayyana cewa bai yi danasanin duk wani mataki da ya dauka na cewa lallai APC reshen jihar Zamfara bata gudanar da zaben fidda gwani ba a watan Oktoban shekarar da ya gabata. 

Marafa wanda karar da ya shigar kotu yayi sanadiyar soke dukkanin zaben fidda gwanin da jam’iyyar ta gudanar a jihar, yace mutanen Zamfara na farin ciki da hukuncin kotun koli da ya kori dukkanin zababben yan APC a jihar. 

Da yake Magana a taron bankwana na majalisar dattawa na takwas a jiya Alhamis, 6 ga watan Yuni, Marafa yace koda dai bai so ace jam’iyyar adawa ta PDP ta amfana daga matakinsa ba, tuna ya amince da hukuncin. “Ban yi danasani kan abunda nayi ba. An haife ni ne domin nayi yaki, kuma zan ci gaaba da yaki. Mutanen jihar Zamfara sun yi farin ciki da abunda ya faru,” inji shi.
 

DAGA ISYAKU.COM

 Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN