Ashsha: Wata budurwa ta kashe kanta bayan sun rabu da saurayinta


Legit Hausa

Wata dalibar jami’ar Benin (UNIBEN), Christabel ta kashe kanta a dakin kwananta dake unguwar Newton, Ekosodin a garin Benin bayan ta sha guba. Wasu majiyoyi sun tabbatar da cewa, marigayiyar ta sha maganin kashe kwari bayan ta hada shi da lemun kwalba, ta kuma bar wasika inda ta bayyana cewa zata kashe kanta saboda saurayinta ya rabu da ita. Amman wata majiya ta kawo cewa an gano ledan sabulun wanki a inda aka tsinci gawarta.

Haka zalika, a wani rubutu a shafin zumunta daga wata ma’aikaciyar UNIBEN, an rahoto cewa wasikar, wanda a halin yanzu ya ke a hannun yan sanda a ofishin yan sanda a Ugbowo, an rubuta ta ne zuwa ga mutane biyu, sannan kuma an gayyace su zuwa ofishin yan sandan don amsa tambayoyi.

 Rubutun yayi ikirarin cewa ba wait a kashe kanta saboda matsalar da ta samu da masoyinta bane kawai illa wasu al’amuran da ta kasa magancewa a tsakaninta da wadannan mutane biyun da ta ambata a wasikar.“Wasikar bai bayyana abunda ya faru ba tsakaninta da mutane biyun da ta ambata, wannan dalilin ne yasa yan sanda suka gayyace su domin su bayyana dalilin da yasa marigayiyar kashe kanta,” cewar rubutun.
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

 Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN