An samu zababben Sanata dan Kwankwasiyya a kasar Gambia


Legit Hausa

Mabiya darikar siyasar Kwankwasiyya dake karkashin jagorancin tsohon gwamnan jahar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na cike da farin ciki biyo naso da manufar darikarsu tayi zuwa wajen Najeriya.

 Legit.ng ta ruwaito a makon data gabata ne aka jiyo Sanata Rabiu Kwankwaso yana bayyana yadda darikar Kwankwasiyya ta samu karbuwa a duk fadin duniya bama cikin Najeriya kadai ba, a cikin wata hira da yayi da manema labaru. 

“Kai bama Kano ba, bama Najeriya ba, hatta kasashen waje akwai yan Kwankwasiyya, nan wani yaro daga kasar Gambia yazo karatu Najeriya a jami’ar Obasanjo ta Bells, sai yaga daliban Kano dayawa yace waya turosu aka ce masa Kwankwaso. 

“Daga nan ya dauki alwashin sai ya sadu dani, haka ya biyoni har Kaduna bayan mun yi wani taro a Abuja, yace ni yake so na sanya masa hular Kwankwasiyya, kuma na sanya masa hularmu, a yanzu haka yaron ya zama dan majalisa a kasar Gambia, dayake majalisa dayace a kasar, tamkar Sanata yake.” Inji shi. 

A yanzu haka Kwankwaso ya isa kasar Gambia domin ganawa da wannan matashi, inda isarsa filin sauka da tashin jirage na kasar dake Banjul ya samu tarbar Sanata Billay G Tunakara, wanda yayi masa rakiya har zuwa masaukinsa.
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN