Legit Hausa
Rundunar 'yan sandan jihar Osun ta kama wani malamin addinin
Musulunci mai suna Alfa Majid Olore, bayan an gano wani gida da yake satar
mutane yana boye a Ibadan babban birnin jihar Oyo.
Jaridar Independent ta bada rahoton an kama Alfa tare da
matarsa da 'ya'yansa da kuma sama da Almajiransa 55, wadanda ke zama a Ita
Baale a cikin garin Ibadan. Haka kuma kimanin mutane 20 rundunar 'yan sanda
suka kama a yankin Ita Baale.
A cewar wani wanda lamarin ya faru akan idonsa, mutanen da
ake zargin an kulle su a ofishin 'yan sanda na Agugu dake garin Ibadan. Mutumin
ya ce, "Shi dai ya san yaga 'yan sanda sun zo gidan malamin dake unguwar
Ita Baale, inda suka kama shi da matarsa da 'ya'yansa da kuma Almajiransa guda
55, sannan kuma an kama wasu mutanen suma a unguwar.
Ban san ainahin abinda suka yi ba a lokacin, amma dai naga
'yan sandan na dukan Malamin kamar baza su barshi da rai ba, daga baya suka
sanya mishi ankwa." A lokacin da yake tabbatar da faruwar lamarin, jami'in
hulda da jama'a na hukumar 'yan sandan jihar, Mista Olugbenga Fadeyi, ya ce har
yanzu hukumar tana bincike akan lamarin domin tabbatar da cewa zargin da ake yi
gaskiya ne.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Tags:
LABARI