An damke masu leken asiri da kaiwa yan bindiga kayayyaki a Sokoto


Legit Hausa

Hukumar sojin Najeriya ta yi arangama da wasu masu yiwa yan bindiga leken asiri da masu kai musu kayayyaki a kasuwan Burkusuma a karamar hukumar Sabon Birnin jihar Sokoto.

Game da cewar kakakin hukumar, Kanal Sagir Musa, ya ce dakarun sojin atisayen Operation HARBIN KUNAMA III sun yi wannan kamu ne a harin bazatan da jami'an soji suka kai wa yan bindigan cikin jihar Sokoto da kewaye ranar 23 ga Yuni, 2019.

Sun kai harin ne bisa ga rahoton leken asirin da suka samu cewa yan leken asirin masu garkuwa da mutanen sun shigo kasuwa siyayya.

Daga cikin wadanda saka kama sune:

(1)   Malam Ibrahim - Shahrarren mai kaiwa yan bindiga labari da kuma amsan kudin fansa (ii) Mallam Ashiru Goni — Shahrarren mai kaiwa yan bindiga kayayyaki ciki da wajen jihar Sokoto (iii) Mamman Taratse — Shahrarren mai sayar da shanun sata a ciki da wajen jihar Sokoto Hakazalika, jami'an sojin sun yi batakashi da da yan bindiga a kauyan Magira bayan samun labari.
(2)   An hallaka yan bindiga da dama kuma an yi rashin soja daya. Ya ce kwamandan 8 Division, Manjo Janar Hakeem Oladapo Otiki, a madadin babban hafsan soji Laftanan Janar Tukur Buratai, ya yabawa sojin kan jajircewan da sukayi wajen samun wannan nasara.
 

DAGA ISYAKU.COM

 Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

 Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN