Legit Hausa
Wasu rahotanni daga Amurka sun bayyana cewa kasar ta kai
wani hari ta yanar gizo (internet) a kan kwamfutocin da dakarun soji na
juyin-juya hali a kasar Iran ke amfani da su wajen sarrafa manyan makaman yaki
da suka hada da makamai masu linzami (nukiliya).
Rahotanninsun bayyana cewa an ai harin ne a ranar Alhamis
bayan shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya canja ra'ayinsa a kan kai
hare-hare a wasu wurare mallakin kasar Iran. Harin da Amurkan ta kai ba zai
rasa nasaba da harbo wani jirgin yakin kasar Amurka mai amfani da na'ura da
kasar Iran ta yi ba a cikin makon jiya da kuma wani harin da aka kai wa jiragen
dakon danyen man fetur na Amurka, wanda ta dora alhakin kai harin a kan kasar
Iran.
Babu wata kafar watsa labarai wacce ba ta Amurka ba da ta
bayar da tabbacin cewa harin ya lalata makaman yakin kasar Ira. Shugaba Trump
dai ya bayyana cewa kasar Iran ta tafka babban kuskure da ta harbo jirgin yakin
kasar Amurka da ake sarrafa wa da na'ura.
Jirgin, maras matuki, da Iran ta harbo na daga cikin jiragen
yaki masu matukar tsada da kasar Amurka ta mallaka. Trump ya bayyana cewa zai
shafe kasar Iran daga doron kasa idan yaki za su yi. Wutar yaki da ke ruruwa
tsakanin kasashen biyu ta jawo zaman dar-dar a kasashen yankin Persia.
Tuni Andrew Murrison, sakataren harkokin kasashen waje na
kasar Birtaniya ya isa kasar Iran domin tatauna wa da shugabannin kasar domin
yi musu sulhu da kasar Amurka. Shugaba Trump ya bayyana cewar a shirue yake ya
yi sulhu da kasar Iran tare da bayyana cewar kasar Amurka a shirye take idan
kasar Iran yaki take so su gwabza. Sai dai, ya gargadi kasar Iran da ta sani
cewa Amurka ba tsarar ta ba ce.
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Tags:
TSARO