Zamfara ta cika da murna bayan hukuncin kotun koli a kan APC


Legit Hausa

Hukuncin kotun koli na soke kuri'un jam'iyyar APC a zaben gwamna na shekarar 2019 a jihar Zamfara ya sanya jama'a da dama murna a garin Gusau babban birnin Jihar Zamafara kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Masu babbura da dama suna ta yawa a titunan Gusau suna yabawa hukuncin kotun yayin da suke dauke da fostocin dan takarar gwamnan na jam'iyyar peoples Democratic Party ( PDP) Dr Bello Mutawalle Maradun. 

Mazauna garin Gusau kuma sun bayyana mabanbanta ra'ayoyi game da hukuncin babban kotun inda wasu da yawa cikinsu su kayi fatan alheri ga gwamnatin da za ta kama aiki nan ba da dadewa ba. "Ina fatan sabuwar gwamnatin za ta inganta rayuwar mutane. 

Banyi mamakin hukuncin kotun ba duba da abubuwan da suka rika faruwa tun daga lokacin da aka fara zabukkan cikin gida zuwa yanzu," inji wani magidancin mai suna Aliyu Hussain.
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN