Yanzu Yanzu: An zabi gwamnan Kebbi a matsayin shugaban kungiyar gwamnonin APC


Legit Hausa

An zabi gwamnan jihar Kebbi, Atiku Bagudu, a matsayin shugaban Kungiyar gwamnonin jam’iyyar APC Legit.ng ta rahoto cewa kungiyar ta bayyana haka ne a shafinta na tweeter a ranar Juma’a, 24 ga watan Mayu. 

An tattaro cewa an zabi Bagudu ne a taron gwamnoni da aka gudanar a Abuja a daren ranar Alhamis, 23 ga watan Mayu, a masaukin gwamna. Bagudu, wanda aka hada kai aka zabe shi, zai maye gurbin Gwamnan jihar Imo, Rochas Okorocha wanda mulkinsa zai kare a ranar 29 ga watan Mayu. 

A halin da ake ciki, Legit.ng ta rahoto a baya cewa an zabi Gwamna Kayode Fayemi, wanda ya kasance tsohon ministan albarkatun kasa a matsayin shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya a lokacin taron kungiyar a Abuja.

An rahoto cewa gwamnan jihar Ekiti ya yi nasara a matsayin wanda aka fi so ya gudanar da harkokin kungiyar bayan gwamnonin sun ki amincewa da gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai.
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN