Legit Hausa
An tabbatar da mukaddashin Sifeto Janar na hukumar yan
sandan Najeriya, Muhammad Adamu, a matsayin sifeto janar na din-din-din a ranar
Alhamis, 22 ga wtaan Mayu, 2019 a fadar shugaban kasa dake birnin tarayya
Abuja.
An tabbatar da IGP Adamu ne a wani taro na musamman da
shugaba Muhammadu Buhari ya jagoranta da kansa. Shugaban ma'aikatan hukumar yan
sanda, Musuliu Smith, da gwamnonin Najeriya 36 ne suka halarci wannan muhimmin
taro.
IGP Adamu ya dau ragamar mulkin hukumar yan sandan ne a 15
ga watan Junairu, 2019 daga hannun magabacinsa, Ibrahim Idris.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi