Yanzu Yanzu: Kungiyar gwamnonin arewa sun zabi shugaba, za su kafa wata kwamitin hadin gwiwa


Legit Hausa

Gwamnan jihar Plateau, Simon Lalong ya zama shugaban kungiyar gwamnonin arewa na wasu shekaru hudu masu zuwa. Takwarorinsa ne suka zabe shi a lokacin taron kungiyar gwamnonin arewa wanda ya gudana a Kaduna a ranar Juma’a, 17 ga watan Mayu. 

A wajen taron wanda shine na farko a shekarar nan, gwamnonin sun amince da kafa wani hukumar kudi na hadin gwiwa wanda zai taimaka wajen kawo ci gaban al’umma da tattalin arziki a yankin sannan hakan zai bayar da damar dogaro da kai ta bangaren kudi.

Gwamnonin sun kuma yanke shawarar ganawa da shugaban kasa Muhammadu Buhari kan matsalolin tsaro a yankin.Ana sanya ran ganawar gwamnonin wanda daga bisani ya shiga sirri, zai samu jawabai akan yanayin tsaro a fadin jihohin da kuma sadaukarwa daga jami’an kamfanin ci gaban arewacin Najeriya kan nasarorin da aka samu a fannin hako mai a tafkin Chadi, da kuma farfado da durkusashen kamfanin buga kayayyaki na Kaduna mallakar jihohin arewa 19.
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN