Yan acaba sun yi kone kone a ofishin Yansanda saboda suna kwace musu kudi


Legit Hausa

Wasu gungun fusatattun yan acaba sun yi zuga zuwa ofishin yansandan Najeriya dake garin Zuba na jahar Neja, inda suka banka ma ofishin wuta tare da kona motocin da yansandan suke amfani dasu wajen gudanar da sintiri. 

Majiyar Legit.ng ta ruwaito yan acaban sun dauki wannan mataki ne bayan cin zarafin guda daga cikinsu da Yansandan suka yi saboda yaki amincewa ya basu kudi, inda yan acaban suka ce sun gaji da cin zalinsu da Yansandan suke yi suna kwace musu kudi. 

Wannan lamari dai ya auku ne da misalin karfe 8 na safe zuwa karfe 10 na safiyar Alhamis, 23 ga watan Mayu, wanda hakan ya janyo zaman dar dar da tashin hankali a yankin, tare da gurgunta hada hadar kasuwanci don tsoron abinda kaje ka dawo. 

Wani dan Achaba dake yankin yace “Yansanda sun sha tare yan acaba suna kwace mana kudi, sun mayar damu tamkar na’urar ATM da take basu kudi a duk lokacin da suka ga dama, don haka muka dauki alwashin ba zamu lamunci wannan cin zali ba, sai dai su kashemu,” Shima kaakakin Yansandan babban birnin tarayya Abuja. 

DSP Anjuguri Manzah ya tabbatar da kai harin tare da kona ofishin Yansandan, inda yace tuni sun kaddamar da bincike akan lamarin, tare da burin kama duk masu hannu a ciki.
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN