Legit Hausa
Jam'iyyar All Progressive Congress (APC) ta jihar Zamfara ta
kasu kashi biyu ne, wato bangaren gwamna mai barin gado Abdul'aziz Yari da kuma
bangaren mataimakinsa da Sanata Kabiru Marafa da Ministan tsaro da kuma Hon
Jaji.
Wutar rikicin siyasar jihar ta samo asali ne a lokacin da
gwamnan jihar Abdulaziz Yari ya nuna goyon bayansa ga kwamishinan kudin jihar,
Alhaji Muktar Shehu Idris, inda ya nuna cewa shine zai hau kujerar gwamnan
jihar idan ya sauka. Hakan ne ya janyo jam'iyyar APC a jihar ta kasa yin zaben
fidda gwani na 'yan takarar gwamna dana 'yan majalisar tarayya da kuma na 'yan
majalisar jiha.
Wannan dalilin ne yasa wasu manya a jihar masu sha'awar
fitowa takarar gwamna a jam'iyyar APC kimanin su takwas kamar irin su
mataimakin gwamnan jihar Ibrahim Wakalla da ministan tsaro na kasa Mansur Dan
Ali suka hada kai guri guda domin su yaki gwamnan.
Sau kusan biyu ana kokarin gabatar da zaben fidda gwani a
jihar, amma a karshe sai a soke zaben saboda rikicin dake tsakanin bangarorin
jam'iyyar guda biyu. A bangaren gwamnan jihar, ya fake da wani sakamakon
hukunci da babbar kotun jihar ta yanke, inda alkalin kotun ya bayyana cewa an
gabatar da zabe ba tare umarnin hukumar zabe ta kasa ba.
Hukuncin da wata babbar kotun tarayya dake Abuja ta yanke,
shine ya tabbatar da matsayin hukumar zabe ta kasa akan haramta wa dukkanin
'yan takarar jam'iyyar APC na jihar yin zabe. Hukuncin da kotun Abujan ta yanke
yayi daidai dana kotun jihar wanda mai shari'a Muhammad Bello Shinkafi ya
yanke.
Sai dai kuma alkalin kotun tarayyar mai shari'a Ijeoma
Ojukwu ta jaddada matsayin hukumar zabe na kasa, inda ta bayyana cewa jam'iyyu
za su cigaba da yin karen-tsaye akan dokokin zabe idan har suka kasa mutunta
ka'idojin da aka kafa na jadawalin zabe.
Alkalin ta ce hukunci da aka yanke din darasi ne ga sauran
jam'iyyun kasar nan a nan gaba. Bayan an daga zaben 2019 ne wata kotu dake
Abuja ta bai wa hukumar INEC umarnin karbar 'yan takarar APC, hakan ne yasa
jam'iyyar APC a Zamfara ta shiga zaben 2019. Sai dai kuma wata kotun daukaka
kara a jihar Sokoto ta yi watsi da hukuncin kotun Abuja, inda hakan ne yasa
bangaren gwamnati ya daukaka kara zuwa kotun koli.
Yanzu haka dai kotun koli ta soke zaben jam'iyyar APC na
jihar baki daya. Akwai alamun irin hakan za ta faru a jihar Kano, inda yanzu
haka ake sauraron karar da dantakarar gwamnan jihar na jam'iyyar PDP Abba Kabir
Yusuf ya shigar, inda yaake neman kotu ta binciki zaben jihar akwai lauje cikin
nadi, musamman ma ganin yadda aka dage zaben wasu kananan hukumomi a jihar.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi