Legit Hausa
An samu gawar wata daliba, Mercy
Naan, mai shekaru 23, dake shekara ta biyu a bangaren karatun kasuwanci, a
dakin kwanan dalibai mai suna 'Zion' a Naraguta. Tun a ranar 3 ga watan Mayu,
iyayen dalibar suka shigar da korafi a ofishin tsaro na jami'ar a kan cewar
diyar su ta bata.
Rundunar 'yan sandan jihar Filato,
ta bakin kakakinta, DSP Tyopev Terna, ta tabbatar da labarin mutuwar dalibar,
ta ce an gano gawar ta ne bayan daliban dake kwana a dakin sun yi korafi da
wani wari mai karfin gaske dake fitowa daga dakin dalibar ranar Lahadi.
Rundunar 'yan sandan ta ce liktoci a
asibitin jami'ar sun tabbatar da mutuwar ta, sannan an ajiye gawar a dakin
ajiya na sashen karatun ilimin sanin sassan jikin bil'adama (Anatomy). Kazalika
ta bayyana cewar ta fara binciken sarkakiyar dake tattare da mutuwar matashiyar
dalibar.
Sai dai, da aka tuntubi mataimakin
rijistaran jami'ar mai kula da bangaren yada labarai da sadarwa, Abdullahi
Abdullahi, ya ce jami'ar na gudanar da bincike domin tabbatar da cewar
matashiyar dalibar makarantar ce ta hakika Abdullahi ya kara da cewa da zarar
hukumar jami'ar ta kammala bincike tare da samu dukkan bayanan marigayiyar, za
a tuntubu iyayenta kafin jami'ar ta fitar da wani jawabi a hukumance.
Ya bayyana cewar matukar ba hakan
jami'ar tayi ba, duk wani jawabi za ta dauke shi ne a matsayin hasashe kawai,
ya kara da cewa hukumar makarantar da hadin gwuiwar hukumomin tsaro za su
gudanar da binciken kwakwaf a kan lamarin
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi