Legit Hausa
Aisha Buhari, uwargidan shugaban kasa Muhammadu Buhari, ta
kausasa harshe dangane da yadda gwamnatin tarayyar Najeriya ta batar da kimanin
Dalar Amurka miliyan 16 wajen tanadar gidajen sauro a kasar nan.
Uwargidan shugaban kasa ta yi magana da kakkausar murya
dangane da yadda gwamnatin Buhari ta batar da Dalar Amurka miliyan 16 wajen
sayen gidajen sauro yayin wani taron karawa juna sani na Mata da aka gudanar
cikin fadar shugaban kasa dake Abuja a ranar Asabar.
Kamar yadda jaridar The Nation ta ruwaito, Aisha Buhari ta
ce shirye-shiryen bayar da tallafi da gwamnatin tarayya ta assassa da manufa ta
inganta jin dadin rayuwar al'umma, SIP (Social Investment Programmes) ba ya da
wani tasiri a yankin Arewacin kasar nan.
Cikin jawaban ta, uwargidan shugaban kasa yayin bayar da
shaidar masaniyar yadda gwamnatin Buhari ta batar da dalar Amurka miliyan 16
wajen sayen gidajen sauro, ta ce kawowa yanzu babu wanda ya ribaci wannan
gidajen sauro musamman a mahaifar ta ta jihar Adamawa.
Duk da mika kokon barar ta da kuma shigar da bukatar neman
nata kason na gidajen sauro domin aikewa al'ummar mahaifar ta, Aisha Buhari ta
ce har ila yau lamarin ya zamto tamkar an aika Bawa garin su.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Tags:
LABARI