Wani jirgin saman yaki na Isra'ila ya yi luguden wuta kan Falasdinawan Gaza


Legit Hausa

A yau Alhamis dinnan ne 2 ga watan Mayu, 2019, jirgin saman yakin kasar Isra'ila ya kai wani mummunan hari kan dakarun Hamas a arewacin Gaza.

Sojojin Isra'ilan sun bayyana cewa sun kai harin ne bayan da wata wuta ta kama a daji kusa da Eshkol da ke yankin kudancin Isra'ila. Rahotanni sun nuna cewa wutar ta kama ne saboda wani abun fashewa da ya fashe a kusa da wani birni na kasar Isra'ila.

 Wasu shaidu 'yan kasar Palasdinu sun bayyanawa kamfanin dillancin labarai cewa jirgin saman ya kai harin kan wani yanki na sansanin sojojin Hamas a arewacin Gaza. Rahotanni sun nuna cewa, ba ayi asarar rai ba, amma an bata abubuwa da dama a sansanin sojojin.

"Sojojin Isra'ila za su cigaba da kashe duk wasu mutane da suka yi yunkurin cutar da al'ummar kasar Isra'ila," in ji rahoton. An kwashe shekaru masu yawan gaske ana samun hare-hare a yankin zirin Gaza.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

 Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN