Shegiyar Uwa: Hukumar Hisbah ta ceto yar jaririyar da mahaifiyarta ta birne da rai


Legit Hausa

Hukumar Hizbah, shiyar jihar Kebbi, ta ceto wata jaririyar yar kwanaki biyu da haihuwa bayan mahaifiyarta ta birneta da rai. An gano gawar yar jaririyar kwana biyu bayan haihuwarta a bayan wani Otal dake cikin garin Birnin Kebbi.

Mahaifiyar yarinyar da wata kawarta sun kama daki a shahrarran Otal mai suna Zinari, na tsawon kwana biyu kuma suka silale suka birne yarinyar cikin dare a bayan Otal. Diraktan bangaren Shari'a da harkokin addinin jihar, Alhaji Abubakar Muhammad Lamne Augie, ya ce kukan yar jaririyar ya jawo hankalin jama'a kuma suka cirota daga inda suka birneta. 

Yace: "Mahaifyar yarinyar ta birne jaririyar da ranta bayan sun zauna a Zinari Hotel na tsawon kwana biyu." Bayan birne jaririyar, sai suka leka ko yarinyar ta mutu. Amma da suka hakota, sai yarinyar ta fashe da kuka, sai suka ruga da gudu.

" Ya ce yarinyar bata daina kuka ba har sai da jama'a suka ji kukan kuma suka ceceta. sai Jama'a cirota daga kasa, sannan suka sanar da hukuma domin ceton rayuwar yarinyar. Kana mazauna unguwar sun shiga cikin Otal din kuma duka damke wadannan yan mata biyu. Tsokaci: Hoton da muka sanya na bayani ne kawai, ba ainihin hoton jaririya bane.
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN