Legit Hausa
Shugaba Muhammadu Buhari na shirin baiwa yan Najeriya a
mamaki a sabuwar gwamnatin da zai nada musamman sabuwar ranar Demokradiyya 12
ga Yuni.
Ana kyautta zaton cewa nan da ranar 29 ga Mayu, wasu sunayen
zasu fara bayyana. Majiyar Aljazirah ta bayyana cewa shugaba Muhammadu Buhari
na shirin nada tsohon gwamnan jihar Legas a zamanin mulkin soja, Janar Buba
Marwa ko kuma tsohon shugaban hukumar hana almundahana da yiwa tattalin arzikin
kasa zabon kasa wato EFCC, Nuhu Ribadu.
Daya daga cikinsu zai maye kujerar Abba Kyari, mai ci a
yanzu. Abinda ya sa Buhari ke tunanin nada Buba Marwa ko Nuhu Ribadu shine a
wannan karon, yana bukatar kwararre ko kuma wanda ya taba aikin soja. Aljazirah
Nigeria, ta tattaro cewa Buba Marwa ne yafi cancanta bisa ga bukatun Buhari
fiye da kowa amma tarihin Nuhu Ribadu kan yaki da cin hanci da rashawa ka iya
sa Buhari ya nada shi.
Wata majiyar daban ta bayyana cewa wandannan mutane guda
biyu ko ta kaka suna cikin mutane biyar da shugaba Buhari zai fara nadawa a
sabbin nade-nadensa guda biyar.
Nade-naden sune shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa,
babban mai baiwa shugaban kasa shawara kan tsaro NSA, sakataren gwamnatin
tarayya, shugaban ma'aikatan gwamnati, da mai magana da yawun shugaban kasa.
Sauran wadanda ka iya samun shiga sune Dame Pauline Tallen,
Gwamna Jibrilla Bindow, Adamawa, Gwamna Mohammed Abubakar, Bauchi, Hon Ahmed
Aliyu Wadada, Nasarawa, da Hon Emmanuel Jime, Benue. Majiya yta bayyana cewa an
tattara wadannan sunaye ne lokacin da shugaban kasan a kai ziyara kasar Ingila.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi