Legit Hausa
Musa Kwankwaso, hakimin karamar hukumar Madobi kuma mahifi
ga tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, ya janye biyayyar
sa ga sarkin Kano Muhammadu Sanusi II. A cikin satin da ya gabata ne gwamnan
Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya rattaba hannu a kan dokar masarauta da
majalisar dokokin jihar tayi wa garambawul.
Daga cikin gyaran da aka yiwa dokar akwai bukatar kara
kirkirar sabbin masarautu hudu da sarakuna masu daraja daya da ta sarkin Kano.
Sabbin masarautun da dokar ta amince da kirkirar su akwai, Bichi, Gaya, Karaye
da Rano. Sabbin Sarakuna: Mahaifin sanata Kwankwaso ya yi biyayya ga umarnin
Ganduje A ranar Asabar ne gwamna Ganduje ya rantsar da sabbin sarakunan
masarautun tare da basu sandar iko, sannan ya umarci duukan masu rike da
sarautar gargajiya da malaman addini da suyi mubaya'a ga sabbin sarakunan
yankin da suka tsinci kan su.
Sabanin wasu masu rike da sarauta da suka yi murabus ko kin
yin biyayya ga sabbin sarakunan, Musa Kwankwaso ya jagoranci kafatanin masu
rike da sarauta dake karkashin sa wajen kai ziyarar yin muba'a da biyayya ga
sabon sarkin Karaye, Ibrahim Abubakar II, da masarautar karamar hukumar Madobi
ta koma karkashin ikon sa. Wannan ziyara ta Musa Kwankwaso ta nuna cewar ya yi
biyayya ga umarnin Ganduje, ya janye biyayyar sa daga tsohuwar masarautar Kano.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi