Rashin tsaro: Majalisar Wakilai ta nemi Buhari ya bayyana a gaban ta


Legit Hausa

Majalisar wakilai ta Najeriya a ranar Alhamis, ta sake gayyatar shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya hallara a farfajiyar zauren ta domin bayyana mata yadda gwamnatin sa ke riko da al'amura na rashin tsaro da suka addabi kasar nan.

Jaridar The Punch ta ruwaito cewa, majalisar wakilai na neman jin ta bakin shugaban kasa Buhari kan yadda gwamnatin sa ke tafiyar da al'amurran kawo karshen kalubalai na rashin tsaro da suka zamto sarkakiya a fadin Najeriya.

Wannan ita ce gayyata ta biyu cikin makonni uku da majalisar ta shigar na neman shugaban kasa Buhari ya hallara gaban ta domin samun karin haske kan babban kalubale na rashin tsaro da ya yiwa kasar nan dabaibayi.

Majalisar yayin zaman ta na ranar 11 ga watan Afrilun 2019, ta shigar da wani kudiri na tursasa shugaban kasa Buhari akan bayyana yadda gwamnatin sa ke tafiyar da al'amurran tsaro tare da gindaya wa'adin kwanaki biyu kacal a kansa.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN