Legit Hausa
Majalisar wakilai ta Najeriya a
ranar Alhamis, ta sake gayyatar shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya hallara a
farfajiyar zauren ta domin bayyana mata yadda gwamnatin sa ke riko da al'amura
na rashin tsaro da suka addabi kasar nan.
Jaridar The Punch ta ruwaito cewa,
majalisar wakilai na neman jin ta bakin shugaban kasa Buhari kan yadda gwamnatin
sa ke tafiyar da al'amurran kawo karshen kalubalai na rashin tsaro da suka
zamto sarkakiya a fadin Najeriya.
Wannan ita ce gayyata ta biyu cikin
makonni uku da majalisar ta shigar na neman shugaban kasa Buhari ya hallara
gaban ta domin samun karin haske kan babban kalubale na rashin tsaro da ya yiwa
kasar nan dabaibayi.
Majalisar yayin zaman ta na ranar 11
ga watan Afrilun 2019, ta shigar da wani kudiri na tursasa shugaban kasa Buhari
akan bayyana yadda gwamnatin sa ke tafiyar da al'amurran tsaro tare da gindaya
wa'adin kwanaki biyu kacal a kansa.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi