NSGF ta kaddamar da wani muhimmin shirin farfado da tattalin arzikin arewa


Legit Hausa

Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, NSGF ta kafa wata gidauniyar kudi a kan Naira biliyan shida domin farfado da tattalin arzikin yankin da kuma kawo cigaba. Shugaban kungiyar mai barin gado, gwamna Kashim Shettima na jihar Borno ne ya bayar da wannan sanarwar yayin da ya ke bitan nasarorin da ya samu a shekaru hudu da suka gabata a ranar Juma'a a Kaduna.

Ya ce an dauki wannan matakin ne domin tabbatar da cewa yankin arewa ya fara dogoro da kansa a fanin samar da kudade. Ya ce a karkashin shirin za a farfado da masakun yankin da kuma kamfanin New Nigeria Development Company (NDDC).

Shettima ya ce ana sa ran gwamnonin jihohin arewa 19 ne za su tattaro kudin da za kamfanin za tayi amfani dashi. A halin yanzu sun tara Naira miliya 650. "Domin cimma burin mu, ko wace jiha za ta rika bayar da gudunmuwar Naira miliyan 50 kowane wata na tsawon watanni shida. 

"A halin yanzu, muna da N560 miliyan a cikin N5.7 biliyan da muke bukata. Ina kira ga jihohin da ba su cika alkawurransu ba da suyi kokarin yin hakan domin su samu damar fara ayyukan da muka tsara a karkashin shirin. 

"Ayyukan sun hada da samar da kamfanin lantarki da zai iya samar da wuta mega watt 3000 zuwa 4000. "Kungiyar kuma ta fara daukan matakan farfado da kamfanin New Nigeria Development Company, NDDC don ya cigaba da aikinsa a matsayin cibiyar kasuwanci da tattalin arziki na yankin arewa," inji shi.
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN