Nade-naden mukamai: Bincike ya nuna Buhari ya fifita kudu sama da arewa


Legit Hausa

Sabanin shahararren hasashen nan da ke yawo, bincike da hujjoji da suka billo sun nuna cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ba yankin kudu manyan mukamai masu maiko a kasar fiye da yanda yayi a arewa. 

Takardu da ke kunshe da nade-naden da Shugaban kasa Buhari yayi a gwamnatinsa na farko a 2015 ya nuna cewa akwai daidaito tsakanin yankunan biyu, jaridar Vanguard ta ruwaito. Misali, jihar Ogun ce a saman jarin mukaman inda take da nade-nade 31, fiye da nade-naden da jihohin arewa maso yamma uku ke dashi wanda suka hada da Kebbi 13, Zamfara bakwai da kuma Sokoto mai shida.

A arewa maso yamma, jihar Katsina ce da mukamai mafi yawa guda 24, yayinda Kaduna da Kano suka samu 16; inda Jigawa ke da 12. Inda a nade-naden siyasa kudu maso gabas ce keda mafi karanci, Imo ce ta uku a nadin MDA (nade-nade 29), sannan aka bai wa Anambra 20 inda Abia ta samu 14. 

Jihohi kamar su Enugu da Ebonyi na da takwas da bakwai. Sai dai kuma, takardu dun nuna cewa yawan nade-naden shugabanni a ma’aikatu, kaso 51 cikin dari ya tafi ne ga jihohin arewa 19, sannan kaso 49 cikin dari ya tafi ga jihohin kudu 17. 

A daya bangaren, manyan nade-naden siyasa 124 kamar irin su masu bayar da shawara na musamman, manyan masu bayar da shawara, da kuma hadimai na musamman ga Shugaban kasa sun kasance 59 daga arewa sannan 65 daga kudu.
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN