Na shiga tseren shugabancin Majalisar Dattawa ne domin in yi nassara - Ndume


Legit Hausa

Tsohon Shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa, Ali Ndume, ya nuna karfin gwiwar cewa zai zamo Shugaban majalisar dattawa ta tara, a wata mai zuwa.

Koda dai jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki ta nuna Sanata Ahmad Lawan ne zabinta a wannan kujera, Ndume ya dogara da goyon bayan takwarorinsa da shugabannin jam’iyyar.

Da yake jawabi ga manema labarai a Lagas, a jiya Litinin, 6 ga watan Mayu, Ndume, wanda yace bai shiga tseren domin yin cinikin kowani mukami mai gwabi-gwabi ba, ya jadadda cewa ya tuntubi Shugaban kasa Muhammadu Buhari, babban jigon APC na kasa, Asiwaju Bola Tinubu da sauran shugabannin jam’iyya mai mulki, akan kudirisa, sannan kuma cewa dukkansu sun sanya masa albarka a kudirinsa.

Ndume ya ci gaba da bayyana cewa, babu wanda ya nemi ya janye ma wani daga tseren. Tsohon Shugaban masu rinjaye a majalisan yace hatta da Shugaban APC na kasa, Adams Oshiomhole, yayi bayanin cewa jam’iyyar dai ta gabatar da Sanata Lawan ne a matsayin dan takarar da tafi so sannan ba wai tana kokarin tursasa shi akan sanatoci bane.

Da yake Magana akan ajandarsa, Ndume wanda a yanzu yake wakiltan Borno ta kudu, yayi alkawarin inganta kokarin da majalisa ta takwas tayi, sannan ya kara da cewa zai rage kwadaitar da mukamin Shugaban majalisar dattawa ga mutane ta hanyar rage wasu abubuwa marasa amfani da ke jingine da kujerar.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

 Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN