Legit Hausa
Kasurgumin mai garkuwa da mutane da ya jagoranci garkuwa da
surukar gwamnan jihar Katsina, Hajiya Hauwa Yusuf, ya bayyana yadda ya karbi
milyan biyu da rabi cikin milyan talatin da suka karba matsayin kudin fansa.
Dan barandan mai suna, Abubakar M. Sani alias Kubi, mazauni
unguwar Sokoto Rima ya ce bayan garkuwa da dattijuwar, sun sayar da ita ga wani
kungiyar masu garkuwa da mutanen da ke dajin Batsari. A cewarsa: "Ban taba
saninta ba.
Na biyo ta unguwan ne kawai na ga a a raba takardun siyasa.
Lokacin da muke saceta, daga daya cikin abokanmu yace ya san wasu yan barandan
a cikin daji kuma muka mikata garesu." "Daga cikin N30m da aka biya
kudin fansa, na samu N2.5m, yayinda sauran abokaina biyu suka samu milyan
biyu-biyu." Kwamishanan yan sandan jihar, Sanusi, ya bayyana cewa Abubakar
Dani alias Dan Bose, Rabe Hamza alias Tankabaje, Marwana Gide, Abdulhakim
Bishir, ne suka sace tsohuwar.
Mun kawo muku rahoton cewa Hukumar yan sandan Najeriya ta
samu nasarar damke wasu masu garkuwa da mutane 13 da suka addabi jihar Katsina
wanda ya kai ga sace surukar gwamnan jihar, Aminu Bello Masari a ranar 8 ga
watan Fabrairu, 2019. Kwamishanan yan sandan jihar Katsina, ya bayyanasu ga
manema labarai a yau Litinin, 20 ga watan Mayu, 2019.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi