Legit Hausa
Fusatattun matasa daga yankin karamar hukumar Batsari na
jihar Katsina a jiya Litinin, 21 ga watan Mayu sun far ma gidan gwamnati da
fadar sarkin Katsina dauke da gawawwakin mutane 18 da aka kashe a harin yan
bindiga.
An kuma tattaro cewa yan bindiga sun kai hare-hare a kananan
hukumomi uku na Jibia, Danmusa da kuma Faskari a jihar. Masu zanga-zangar,
wadanda suka kasance da yawa, sun tuka Babura da motoci biyar, inda suka zargi
jami’an tsaro da aka tura yankinsu da gaza kare su.
Sun kuma bayyana cewa yan bangan sa kai da ke yankin sun fi
su yin kokari a yankin. Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa rikicin ya fara ne
a kauyen Yar Gamji da ke karamar hukumar Batsari lokacin da yan bindigan suka
tuko babura suka kashe wasu manoma a safiyar ranar Talata yayinda suke kakkabe
gonakinsu a shirinsu na shiga aikin noma bayan ruwan sama da aka kwarara cikin
dare.
Al’umman sun ce sun nemi taimako amman babu jami’in tsaro da ya kawo
agaji a lokacin.
Yan mintoci bayan lamarin ya auku, motar yan sanda ta iso
kauyen, ta dauki gawawwakin wadanda aka kashe zuwa fadar mai garin Ruma. Wannan
ya yiwa matasa a yankin zafi, wanda hakan yayi sanadiyar gudanar da zanga
zanga.
Matasan sun daukaka zanga-zangar su zuwa reshen hedikwatar
rundunar yan sanda dake yankin, wanda hakan ya tunzura yan sandan suk kore su,
inda aka harbi mutane uku daga cikin masu zanga zangan.
Wannan ya cigaba da
tayar da hankalin matasan kuma suka yanke shawaran kai gawawwakin babban birnin
jihar yayinda suka cigaba da zanga zangar.
Yayin da yake magana a Gidan Gwamnati , kakakin masu
zanga-zangar Aminu Runa yace sun dauki matakin ne don janyo hankula akan kisa
da ake cigaba da kai wa kauyukansu sannan kuma suna bukatar a samar da
ingantaccen tsaro daga yan bindiga.
Yace ayyukan noma sun ja baya a yankunan kamar yanda mutane
ke tsoron ziyartan gonakin su. Gwamna Aminu Bello Masari yace gwamnatin sa tayi
matukar damuwa da lamarin kashe kashe da yan bindiga ke daukakawa.
Har ila yau yayi kira ga masu zanga zangar dasu kwantar da
hankali, ya bada tabbaci ga matasan cewa gwamnati tana matukar aiki don ganin
ta magance lamarin.
A cewar shi, nadin da aka yi mishi kwanan nan a matsayin
shugaban kwamitin tsaro na kungiyar gwamnonin arewa ya kasance mataki da zai
kawo karshen ta’addanci.
Yayi kira ga al’umma da su nuna aminci ga hukumomin
tsaro su kuma nuna tarayya da hadin kai dasu wajen yakan ta’addanci.
An fahimci cewa hare haren Jibia, Dan Musa da Faskari ne
yayi sanadiyan kisan mutane da dama. Mutane biyar ne aka rahoto an kashe a
kauyen Mara Zamfara (Dan Musa) yayin da aka sace dabbobi da dama. Al’umman
kauyen sun ce yan bindigan sun kai hare hare ga manoman dake aiki a gonaki. A
Sabon Layin Galadima (Faskari), al’umma sunce mutane 11 na aka kashe.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi