Legit Hausa
Hukumar hana yiwa tattalin arziki
ta'annati ta EFCC, ta samu nasarar kwato kadarori 214 cikin garin Abuja, Legas,
Kaduna, Katsina, Jigawa, Kogi, Adamawa, Oyo da kuma wasu jihohi daban-daban a
tsakanin shekarar 2015 zuwa 2018.
Hukumar mai fafutikar hana yiwa
tattalin arziki zagon kasa bisa ga umurnin Kotu, ta samu nasarar kwato kadarori
da dama daga hannun barayin gwamnatin fiye da saba'in a fadin kasar sakamakon
miyagun laifuka masu nasaba da yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati.
Cikin binciken da manema labarai na
jaridar The Punch su ka gudanar a ranar Juma'ar da ta gabata ya tabbatar da
cewa, hukumar ta samu nasarar kwace kadarori daga hannu barayin gwamnati da
suka hadar da; Ima Niboro, kakakin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan.
Sauran mashahuran 'yan Najeriya da
suka rasa mallakin kadarorin su bisa ga umurnin kotu sun hadar da; tsohuwar
Ministan man fetur Diezani Alison Madueke, tsohon shugaban mai bayar da shawara
kan harkokin tsaro na kasa, Sambo Dasuki, tsohon Minista Iyorchia Ayu.
Tsohon shugaban ma'aikatan dakarun
tsaro, Marigayi Alex Badeh, tsohon shugaban hafsin dakarun sojin sama, Air
Marshal Adesola Amosu, tsohon gwamnan jihar Ekiti Ayodele Fayose, tsohon
gwamnan jihar Bauchi Isa Yuguda, tsohon gwamnan jihar Katsina Ibrahim Shema da
kuma Kanal Bello Fadile.
Jerin sunayen ya hadar da George
Turner, wanda kotu za ta kwace kadarorin sa 17 cikin sassa daban-daban a jihar
Bayelsa, tsohon gwamnan jihar Neja Babangida Aliyu da kuma Garba Birnin Kudu
wanda za a kwace kadarori 14 da suka mallaka. Kazalika hukumar EFCC ta kwace
kadarori uku a garin Abuja mallakin Emmanuel Ozigi da wasu mutane biyu.
Hukumar ta kuma samu nasarar a kan
wasu kadarori shida cikin sassa daban-daban a jihar Oyo mallakin wani Oni
Ademola. Jaridar Legit.ng ta fahimci cewa, hukumar EFCC ta kwace kadarori na
alfarma da dama a jihohin Legas, Ribas da kuma Abuja mallakin tsohuwar Ministan
man fetur a gwamnatin tsohon shugaban kasa Jonathan.
Cikin ire-iren kadarori na biliyoyin
Naira da kotu ta bayar da umurnin kwace mallakin su daga hannun masu yiwa
tattalin arziki ta'annati sun hadar da gidaje, masana'atu, gonaki, asusun ajiya
na bankuna daban-daban da makamantan su.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi