Kotu ta kara kwace kujerar majalisar wakilai daga hannun APC, ta umar INEC ta bawa PDP


Legit Hausa

A ranar Litinin ne wata kotun gwamnatin tarayya dake zamanata a Owerri ta yanke hukuncin karbe kujerar majalisar wakilai ta mazabar Nkwerre/Nwangele/Njaba?Isu daga hannun Ugonna Ozurigbo, dan takarar da aka bawa shaidar ya ci zabe a karkashin inuwar jam'iyyar APC. 

A sakin makon da ya gabata ne Ozurigbo ya yi murabus daga mukaminsa na mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Imo. Da yake yanke hukunci, Alkalin kotun, Jastis P. A. Rigime, ya umarci hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC) da ta janye shaidar cin zaben da ta bawa Ozurigbo tare da mika ta ga Kingsley Echendu, dan takarar jam'iyyar PDP. 

Jam'iyyar PDP da dan takarar ta basa cikin wadanda suka shigar da kara kotu a kan zaben Ozurigbo. Kotun ta bayyana cewar Hariison Nwadike, wanda ya shigar da kara, ne halastaccen dan takarar da ya lashe zaben fidda 'yan takara na mazabar da jam'iyyar APC ta gudanar. 

Nwadike ya shigar da karar jam'iyyar APC da hukumar zabe a kan gabatar da sunan Ozurigbo ga masu zabe a matsayin dan takara bayan shine wanda ya lashe zaben cikin gida. Saidai, bayan kotun ta yanke wannan hukunci, Nwadike ya shaida wa manema labarai cewar duk da ya amince da hukuncin kotun a kan cewar shine halastaccen dan takara, kuskure ne kotun ta bayyana dan takarar jam'iyyar PDP a matsayin wanda ya yi nasara. 

Ya kara da cewa zai daukaka kara domin kalubalantar bangaren hukuncin kotun da ya bayyana a mika kujerar ga dan takarar PDP, ya na mai bayyana cewar kamata ya yi kotun ta bashi kujerar tunda dai shine halastaccen dan takarar jamiyyar APC, wacce jama'a suka zaba
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN