Legit Hausa
Jarumar Kannywood, Hadiza Aliyu Gabon ta karyata cewa
rundunar 'yan sanda na jihar Kano ta kama ta saboda ta ki amsa gayyatar kotu. A
hirar da Gabon tayi da Daily Trust a ranar Talata, ta ce babu gaskiya cikin
labarin kuma wasu ne da ke son bata mata suna a idanun jama'a suka kirkiri
labarin.
A baya, Legit.ng ta kawo muku rahoton cewa jarumin Kannywood
Mustapha Badamas Nabraska ya shigar da takwararsa Hadiza Gabon kara a wata
kotun majistare inda ya ke zargin ta da cin zarafinsa. A lokacin Alkalin kotu,
Muntari Dandago ya bayar da umurnin kwamishinan 'yan sandan jihar Kano,
Mohammed Wakili ya kamo Gabon saboda kin amsa gayyatar kotu.
Amma Gabon ta ce, "Yan sanda ba su kama ni ba, rahoton
karya ce tsantsagwaronta da aka kirkira domin a bata min suna. "A halin
yanzu da na ke magana, munyi sulhu da Nabraska da ya kai ni kotu. Saboda haka
ban san inda aka samo labarin kama ni ba. Kotu ta janye umurnin tuntuni,"
inji ta.
Gabon wacce za ta cika shekaru 30 a duniya a watan Yuni ta
kuma karyata labarain da wata kafar yada labarai ta wallafa na cewa ta durkusa
ta nemi afuwar Nabraska sannan ya yafe mata ya janye karar. Ta ce,
"labarin karya ne, ban durkusa wa gaban sa ba (Nabraska); mun zauna ne mun
tattauna mu kayi sulhu a wajen kotu.
" Gabon wacce ta fito a fina-finan 'Jarumta', 'Gida da
Waje' da 'Ciki da Raino' ta bukaci kafafen yada labarai su rika tabbatar da
gaskiyar labari kafin su wallafa ta.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi