Legit Hausa
Wasu Bayin Allah a Najeriya sun fito
sun yi kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya zakulo wasu daga cikin
Ministocinsa wannan karo daga wajen jam’iyyar sa ta APC mai mulkin kasar. Kamar
yadda mu ka samu labari daga Jaridar Punch, wasu ‘yan gwagwarmaya da masana a
kasar nan ne su kayi wannan kira ga shugaban kasa Buhari, a daidai lokacin da
ake shirin kafa sabuwar gwamnati mai-ci a kusan fadin Najeriya.
Moshood Erubami, wanda shi ne
shugaban kungiyar ‘Nigeria Voters Assembly’, ya nemi shugaba Buhari ya zabo
wasu daga cikin wadanda yayi takarar kujerar shugaban kasa da su a zaben 2019,
ya ba su ofishin Minista a gwamnatinsa.
Erubami yake cewa akwai ‘Yan takarar
da bai kamata Buhari yayi watsi da su ba domin zai ga aiki da cikawa idan ya ba
su mukami. Daga cikin wadanda ake rokon a ba mukami akwai Oby Ezekwesili,
Kingsley Moghalu da Yele Sowore.
Wani Malamin harkar siyasa a wata
jami’a a Jihar Ogun, Femi Otunbajo, ya bayyana cewa duk da abu ne mai kyau
shugaba Buhari ya zakulo Ministocinsa daga wajen APC, sai dai zai yi wahala
‘Yan PDP su karbi tayin Minista daga Buhari.
Farfesa Femi Otunbajo, yake cewa
ganin yadda Abokin hamayya, Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP ya shigar da kara a
kotu yana ikirarin cewa shi ne ya lashe zaben bana, zai yi wa manyan ‘Yan adawa
su yarda su yi aiki a gwamnatin APC.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi