Legit Hausa
Wasu yan bindiga sun hallaka akalla mutane 17 a mumunan
harin da suka kai kauyukan Zamfara uku dake karamar hukumar Birnin Magaji dake
jihar Zamfara, Daily Trust ta samu rahoto.
Mazaunan sun bayyana cewa yan bindiga sun shigo garin kan
babura ne ranar Asabar inda suka kai hari kauyan Gidan Kaso kuma suka kashe
akalla mutane 7, sannan kuma suka hana gudanar da jana'izar matattun. Wani
mazaunin garin, Tukur Yusuf, ya laburta cewa:
"Sun hana jama'a gudanar da Sallar Jana'izar matattun
har sai lokacin da jami'an tsaro da yan banga suka kawo agaji kauyen."
Gabanin yanzu mazauna Gidan Kaso sun gudu daga muhallansu
sakamakon hare-haren yan bindiga amma suka dawo kwanan nan. Hakazalika, yan
bindigan sun kai farmaki kauyen Dambo ranar Lahadi inda suka hallaka mutane 4
kuma suka kwashe musu awaki.
Wani mai idon shaida yace: "Mutane bakwai daga kauyen
Kokeya da suka kawo agaji kauyen Dambo sun gamu da ajalinsu a hannun yan
bindigan.
An kashesu yayinda suka kokarin taimakawa wadanda harin ya
shafa a garin Dan Dambo. An nemi jawabi daga bakin kakakin hukumar yan sandan
jihar amma ba'a samu isa gareshi ba yayin wannan rahoto.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi