IGP ya isa majalisar dokoki, ya jero wa majalisar dattawa bayani kan tsaro a ganawar sirri


Legit Hausa

A yanzu haka, Mukaddashin Sufeto Janar na yan sanda, Moammed Adamu na cikin zauren majalisar dattawa, inda yake koro wa yan majalisar tarayya jawabai akan halin da tsaron kasar ke ciki. Jaridar Daily Sun ta ruwaito cewa Adamu ya fara ziyartan ofisin babban mai ba shugaban kasa shawara a harkokin majalisar dokoki (majalisar dattawa), Ita Enang.

Legit.ng ta tattaro cewa yan majalisar sun gayyaci IGP da farko sakamakon halin da tsaron kasar ke ciki. Wannan shine karo na farko da shugaban yan sanda mai ci ya gurfana a gaban majalisar dattawa tun 2014.

Ku tuna cewa Legit.ng ta ruwaito cewa Inspekto Janar na yan sanda, Mohammed Adamu a ranar Alhamis, 25 ga watan Afrilu ya janye tsarin rabe-raben aiki na rundunar yan sandan Najeriya.

A halin da ake ciki, Legit.ng ta rahoto a baya cewa, Wasu kungiyoyi biyu dake rajin tabbatar da mulki nagari a Najeriya, CD da CACOL sun ce matukar gwamnatin tarayya ta bar harkokin tsaro a yankin arewa maso yamma suka cigaba da tabarbarewa, babu shakka nan ba da dadewa ba 'yan bindiga zasu kai wa shugaban kasa Muhammadu Buhari hari ko kuma ma su sace shi.

Kungiyoyin biyu sun bayyana hakan ne a wata hira daban-daban da jaridar Punch tayi da su. Shugaban kungiyar CD na kasa, Usman Abdul, ya ce, "bari na fada muku, da a ce shugaba Buhari ya na garin Daura ranar da 'yan bindiga suka kai hari, zasu iya sace shi."

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN