Legit Hausa
Hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa wato NDLEA
ta gargadi kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano Muhammadu Wakili kan ya fita daga
sha’anin yaki da fataucin miyagun kwayoyi ko kuma ya fuskanci hukuncin shari’a.
Kwamandan hukumar a jihar Kano, Ibrahim Abdul yace, “ sashe
na 3 (1) na kundin dokokin hukumar NDLEA ya basu damar kasancewa jagoran
dukkanin al’amura da suka shafi tu’ammali da muggan kwayoyi a Najeriya.”
Wannan rashin jituwar dai ya zo ne sakamakon furucin da
kwamishinan yayi na cewa jami’an ‘yan sanda sun yi nasarar damke kwalayen
tramadol 303 cikin makon da ya gabata a jihar Kano.
Da yake zantawa da manema labarai ranar Talata, Abdul yace
‘yan sanda sun karbe wani magani mai suna “diclofenac” wanda ke maganin ciwo
jiki amma ba tramadol ba. Kazalika, Abdul ya kara fayyace mana cewa irin hakan
ya taba faruwa a watan Fabrairu inda hukumar yan sanda tayi ikirarin cewa ta
karbe kwayar tramadol, ko da muka bincika sai muka samu ashe maganin zazzabin
cizon sauro ne da wani makamancinsa.
“ Irin hakan ya taba faruwa a watan Fabrairu inda yace sun
kama mota biyu na tramadol. Ko da muka same shi sai yace mana ya tura da su
zuwa NAFDAC. Da isar mu NAFDAC sai muka tarar da abu daban da wanda ya fada
mana.
“ Babu saniyar ware a shari’a ko ni idan na karya doka dole
shari’a zatayi hukuncin mafi dacewa a kaina. Saboda haka ina kira ga hukumar
yan sanda da sauran hukumomi da kowa ya tsaya matsayinsa banda wuce gona da iri
yayin gudunar da ayyukansu.” Inji kwamandan.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Tags:
LABARI