Legit Hausa
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Rundunar tsaro na sirri (DSS) ta saki shahararren malamin
nan, Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi wanda ta tsare bayan ya amsa wasu yan
tambayoyi da tayi masa. Malam Abdulaziz wanda ya kasance babban limamin
Masallacin Juma’a na Dutsen Tanshi da ke Bauchi, ya shiga hannun DSS ne a ranar
Juma’ar da ta gabata.
Daya daga cikin mambobin majalisar daliban malamain,
Muhammad Abdulkadir ya tabbatar das akin Malamin nasu a yau Juma’a, 17 ga watan
Mayu. Ya kara da cewa, wannan kamun da aka yi wa Malaminsu zai kara masa daukake
ne ma a idon duniya ba kuma tauye masa kimarsa ba.
Muhammad Abdulkadir ya bayyana cewar zuwa yanzu dai ba su da
wata masaniya kan ko hukumar tsaron ta gindaya wa Malaminsu wasu sharuda, ya
dai tabbatar da cewar an sako shi kuma ya dawo cikin iyalansa lafiya ba tare da
wani matsala ba.
A baya mun ji cewa, hukumar tsaro ta sirri, DSS, ta yi ram
da wasu manyan Malaman addinin Musulunci a jahohin Katsina da Bauchi, Sheikh
Aminu Usman inkiya Abu Ammar da kuma Ustaz Idris Abdulaziz biyo bayan gayyatar
da hukumar tayi musu.
Majiyar Legit.ng ta ruwaito kimanin kwanaki biyar da suka
gabata ne hukumar DSS ta gayyaci Ustza Idris zuwa ofishinta dake jahar Bauchi
domin amsa wasu tambayoyi, sai dai daga nan kuma suka yi awon gaba dashi zuwa
babban birnin tarayya Abuja don cigaba da yi masa tambayoyi.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi