Legit Hausa
Rundunar hukumar tsaro ta sirri, DSS, ta yi ram da wasu
manyan Malaman addinin Musulunci a jahohin Katsina da Bauchi, Sheikh Aminu
Usman inkiya Abu Ammar da kuma Ustaz Idris Abdulaziz biyo bayan gayyatar da
hukumar tayi musu.
Majiyar Legit.ng ta ruwaito kimanin kwanaki biyar da suka
gabata ne hukumar DSS ta gayyaci Ustza Idris zuwa ofishinta dake jahar Bauchi
domin amsa wasu tambayoyi, sai dai daga nan kuma suka yi awon gaba dashi zuwa
babban birnin tarayya Abuja don cigaba da yi masa tambayoyi.
Wani daaga cikin almajiran Malam ya bayyana cewa tun ranar
Asabar din data gabata basu samu damar tattaunawa dashi ba balle su san halin
da yake ciki. Sai dai shugaban daliban Malam na majalisin Dutsen Tanshi Majlis
Foundation Malam Yau Idris yace: “Duk wani mutum ko kungiya da ta shiga tayar
da hankali ko rikici a dalilin kama Malam da DSS tayi bata tare damu, kuma bada
izinin majalisinmu ko izinin Malaminmu Idris Abdulaziz Bauchi itayi hakan ba,
ko wanene kuwa.” Inji shi.
Shi kuwa Malam Abu Ammar ya shiga hannu ne bayan hukumar DSS
ta gayyaceshi zuwa ofishinta a ranar Talata, 14 ga watan Mayu bayan wani wa’azi
da yayi yana sukar gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari game da
tabarbarewar tsaro a Najeriya.
Abu Ammar yana tare da wani abokinsa mai suna Malam Shamsu a
lokacin da DSS suka kirashi a waya suna gayyatarsa zuwa ofishinsu dake kan
hanyar Daura a garin Katsina, sai suka tafi tare da Shamsu, amma daga bisani
suka nemi Shamsu ya tafi yayin da ake gab da shan ruwa. Idan za’a tuna hukumar
DSS ta taba kama Malam Abu Ammar a watan Maris shekarar 2015 biyo bayan wasu
kalamai daya furta akan tsohon gwamnan jahar Katsina, Ibrahim Shehu Shema.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi