Diyar Mai Martaba Sarkin Kano Muhammad Sanusi na 2 Gimbiya Shahida ta caccaki Gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Ganduje a shafinta na Instagram, duk da yake an cire wannan rubutu amma yaruwarta Gimbiya Fulani Siddika ta sake tura bayanin a yanar gizo.
Shahida ta ruwaito cewa " Idan kuna son ku gani me rashin asali ke jawowa ku duba ku gani abin da ganduje ke yi a Kano. Mutumin da baya da kima yana neman ya wulakantar da abin da ke da kima. Na roki kada Allah ya sa Mahaifiyata ta ce in cire wannan rubutu, domin da bukatar in bar rubutun.Ganduje ne babban bala'i da Allaha ya turo jihar Kano. Duk ababen da yake ta yi abin kyama ne, bakin ciki da son kai. Abin kunya, bama bukatar irin wannan gwamnati. Wallahi muna bukatar gwamnatin da ta fi wannan. Allah ya raba mu da masifar Ganduje, dan kuwa ashe mutane da basu da komi suna irin waannan barna, Ahir".
Tun bayan lokacin da mahaifinata, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya kuduri niyyar kirkirar sababbin masarautu guda hudu, ta dinga yin rubutu da tura bidiyo kala-kala a shafukanta na sada zumunta.
"Tun da can akwai
Sarakunan Rano, Gaya da Karaye sama da shekaru 1000 da suka shude. Rano na daya
daga cikin garuruwan da Shehu Usman Danfodio ya turo mayakanshi domin su kwato
ta, shekaru hudu bayan bayan fulani sun kwace Kano a shekarar 1807. Hakazalika
Rano na daya daga cikin garuruwan 'Hausa Bakwai'. Hakan da aka yi ba komai bane
illa adalci ga garuruwan da aka tauye musu hakkinsu a baya."
NB: Afuwan, Gimbiya Shahida ce ta yi wannan rubutu ba Siddika ba. Da fatan za a fahimce mu. Mun gode.
NB: Afuwan, Gimbiya Shahida ce ta yi wannan rubutu ba Siddika ba. Da fatan za a fahimce mu. Mun gode.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi