Legit Hausa
Mun samu labari cewa fitaccen ‘Dan
majalisar da ke wakiltar mazabar Kaduna ta tsakiya a majalisar dattawan
Najeriya a yanzu, Shehu Sani, ya fito ya tabbatar da maganar da sojojin
Najeriya su kayi kwanaki a game da ‘yan bindiga.
Sanata Shehu Sani yace maganar da
Sojin kasar su kayi na cewa Miyagun da su ka addabi jama’a su na barin kuryar
Arewa maso Yammacin kasar su na dumfarar jihohin Neja da kuma Kaduna mai
makwabtaka da ita, a halin yanzu.
‘Dan majalisar yace babu shakka wannan
labari gaskiya ne domin kuwa Mutanen da ke zama a jejin Kamuku da kuma Alawa
sun bayyana masu wannan. Shehu Sani ya nuna cewa babu karya a maganar da
jami’an tsaron su kayi.
A shafin sa na Tuwita, Sanatan ya
nemi jami’an tsaro su yi maza su yi maganin wadannan ‘yan bindiga da su ke
hallaka mutane babu gaira-babu dalili, kafin su dura cikin wajen babban birnin
tarayya Abuja da ke kan iyaka da jihar Neja.
Jami’an tsaro na Soji sun ce ‘Yan
bindigan da aka fatattako daga cikin Zamfara su na samun mafaka ne a Kaduna,
Kano da kuma jihar Neja, bayan dakarun musamman na Operation Harbin Kunama III
sun lallasa wadannan Miyagu.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Tags:
LABARI