Dole a takawa ‘Yan bindiga burki kafin su shigo Abuja – Shehu Sani



Legit Hausa

Mun samu labari cewa fitaccen ‘Dan majalisar da ke wakiltar mazabar Kaduna ta tsakiya a majalisar dattawan Najeriya a yanzu, Shehu Sani, ya fito ya tabbatar da maganar da sojojin Najeriya su kayi kwanaki a game da ‘yan bindiga.

Sanata Shehu Sani yace maganar da Sojin kasar su kayi na cewa Miyagun da su ka addabi jama’a su na barin kuryar Arewa maso Yammacin kasar su na dumfarar jihohin Neja da kuma Kaduna mai makwabtaka da ita, a halin yanzu.

‘Dan majalisar yace babu shakka wannan labari gaskiya ne domin kuwa Mutanen da ke zama a jejin Kamuku da kuma Alawa sun bayyana masu wannan. Shehu Sani ya nuna cewa babu karya a maganar da jami’an tsaron su kayi.

A shafin sa na Tuwita, Sanatan ya nemi jami’an tsaro su yi maza su yi maganin wadannan ‘yan bindiga da su ke hallaka mutane babu gaira-babu dalili, kafin su dura cikin wajen babban birnin tarayya Abuja da ke kan iyaka da jihar Neja.

Jami’an tsaro na Soji sun ce ‘Yan bindigan da aka fatattako daga cikin Zamfara su na samun mafaka ne a Kaduna, Kano da kuma jihar Neja, bayan dakarun musamman na Operation Harbin Kunama III sun lallasa wadannan Miyagu.


DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN